Sunday, 9 April 2017

Matar Da Ta Haifi Jarirai Hudu A Jihar Bauchi Na Neman Taimako


Assalamu Alaikum wannan mata mai suna HUZAIFATU wacce Allah ya albarkace ta da haihuwar Jarirai guda hudu a garin Chibiyayi karamar hukumar Zaki, dake jihar Bauchi ranar Juma'a 31/03/2017 suna bukatar taimako kasancewar mijin ba mai karfi bane.
Domin tun daga haihuwar har kawo yanzu Huzaifatu da jariranta suna kwance a Asibitin FMC Azare suna karbar magani.
Na ziyarce su jiya na gabatar musu da wani taimako amma har yanzu suna bukatar taimako wanda ya hada da kudin sayen magani, abinci mai gina jiki, madarar jarirai da sauransu.
Ana iya taimakawa ta hanyar Mahaifin jariran Malam Saidu Chibiyayi 08079750567
Sai kuma ni da na yi rubutun 08036802500
Ko kuma a ziyarce su a bangaren haihuwar dake FMC Azare.
Allah ya bada ikon taimakawa amin,
Ismail Muhammad Jauro
8th April 2017



No comments:

Post a Comment

Duk Dan Majalisar Da Ya Yi Yunkurin Tsige Buhari A Bakacin Kujerarsa, Cewar Sanata Kwankwaso

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma tsohon ministan tsaro kuma sanatan Kano ta tsakiya a yanzu, Sanata Dakta Rabi'u Musa Kwankwaso yace...