An yi kira da babbar murya ga Shugaban kasa Muhammad Buhari da cikin gaggawa ya hanzarta sallamar Shugaban hukumar fitar da kayayyaki ta Nijeriya Mista Gbenga Kuye daga kan mukaminshi, biyo bayan Wa'adin shugabanci na shekaru hudu na shugaban sun rigaya sun kare tun a bara, sannan har yanzu yana kan kujerar tare da cigaba da yin zagon kasa ga muradun kasa.
Gamayyar kungiyoyin cigaban matasan yankin arewacin tarayyar Nijeriya
ne sukayi wannan kiran, a yayin wani taron manema labarai na gaggawa da
suka kira, Wanda ya gudana a Otel din Tervan dake garin Kaduna.
Da yake jawabi a yayin taron manema labaran, Shugaban Kungiyar cigaban matasan arewacin Nijeriya na kasa baki daya Alhaji Imrana Nas ya bayyana cewar kiran nasu ya zamo wajibi ne bisa ga la'akari da yadda al 'amura ke wakana a wannan ma'aikata da kuma kokarin yin karfa karfa akan kujerar shugabanci da Mists Gbenga yakeyi ,inda yayiwa Majalisar Tarayya karyar cewar ya shiga office ne a cikin shekarar 2013 alhali a shekarar 2012 ya shiga office kuma Wa'adin shugabancin shi ya kare tun a Watan Disambar Bara.
Matasan Arewan sun kara da cewar da akwai wasu mayan hukumomi biyu wadanda ke karkashin Ma'aikatar ciniki da kasuwanci wanda suka hada da hukumar sarrafa Sukari ta Tarayya NSDC da kuma hukumar fitar da iskar Gas OGEFZA wadanda tuni suka mika ragamar shugabancin hukumomin nasu ga manyan sakatarorin hukumar biyo bayan kammala wa'adin shugabancin su, amma Mista Gbenga Kuye yayi kunnen uwar shegu da dokar kasa, lallai ya kamata Baba Buhari ka dauki matakan da suka dace a kanshi, inji matasan.
Matasan Arewan sun c igaba da cewar a fili yake Mista Koye yana ha'inta da zalunci ga yankin Arewa, domin a shekaru hudu da suka gabata sau biyu ne kawai Gbenga ya ziyarci reshen hukumar dake Kano, wanda rashin halartar tashi ya haifar da gagarumar matsala wajen cigaban 'yan kasuwa da sauran ma'aikatan hukumar dake shiyyar inda yasa wannan shiyya ta tafka asara kuma da gangan ya aikata haka, hakanan Mista Koye ya soke lasisin kamfanin samarwa da fitar da kayayyakin amfaninn Gona ta SEBORE dake Melwa Yola Jihar Adamawa wanda hakan ya haifar da gagarumar asara ga kamfanin da kuma Jama'ar yankin.
Matasan Arewan sun kara da cewar ba suna sukan Gbenga Koye a matsayinshi na dan kudancin Nijeriya bane, saidai suna magana ne akan a tabbatar ana bin tsari da kuma dokokin kasa, Tsohon Shugaban kasa Jonathan ya nadashi shugaban wannan hukumar a shekara ta 2012 domin yin shugabanci na tsawon shekaru hudu, saboda wa'adin shugabancin shi ya kare ne a ranar 24/12/16, sannan an nadashi ne domin yiwa kasa baki daya aiki, ba wani bangare na kasa ba, sai gashi yana cutar da yankin Arewa, ya zama wajibi Shugaba Buhari ya dauki matakan dakatar dashi.
Da yake jawabi a yayin taron manema labaran, Shugaban Kungiyar cigaban matasan arewacin Nijeriya na kasa baki daya Alhaji Imrana Nas ya bayyana cewar kiran nasu ya zamo wajibi ne bisa ga la'akari da yadda al 'amura ke wakana a wannan ma'aikata da kuma kokarin yin karfa karfa akan kujerar shugabanci da Mists Gbenga yakeyi ,inda yayiwa Majalisar Tarayya karyar cewar ya shiga office ne a cikin shekarar 2013 alhali a shekarar 2012 ya shiga office kuma Wa'adin shugabancin shi ya kare tun a Watan Disambar Bara.
Matasan Arewan sun kara da cewar da akwai wasu mayan hukumomi biyu wadanda ke karkashin Ma'aikatar ciniki da kasuwanci wanda suka hada da hukumar sarrafa Sukari ta Tarayya NSDC da kuma hukumar fitar da iskar Gas OGEFZA wadanda tuni suka mika ragamar shugabancin hukumomin nasu ga manyan sakatarorin hukumar biyo bayan kammala wa'adin shugabancin su, amma Mista Gbenga Kuye yayi kunnen uwar shegu da dokar kasa, lallai ya kamata Baba Buhari ka dauki matakan da suka dace a kanshi, inji matasan.
Matasan Arewan sun c igaba da cewar a fili yake Mista Koye yana ha'inta da zalunci ga yankin Arewa, domin a shekaru hudu da suka gabata sau biyu ne kawai Gbenga ya ziyarci reshen hukumar dake Kano, wanda rashin halartar tashi ya haifar da gagarumar matsala wajen cigaban 'yan kasuwa da sauran ma'aikatan hukumar dake shiyyar inda yasa wannan shiyya ta tafka asara kuma da gangan ya aikata haka, hakanan Mista Koye ya soke lasisin kamfanin samarwa da fitar da kayayyakin amfaninn Gona ta SEBORE dake Melwa Yola Jihar Adamawa wanda hakan ya haifar da gagarumar asara ga kamfanin da kuma Jama'ar yankin.
Matasan Arewan sun kara da cewar ba suna sukan Gbenga Koye a matsayinshi na dan kudancin Nijeriya bane, saidai suna magana ne akan a tabbatar ana bin tsari da kuma dokokin kasa, Tsohon Shugaban kasa Jonathan ya nadashi shugaban wannan hukumar a shekara ta 2012 domin yin shugabanci na tsawon shekaru hudu, saboda wa'adin shugabancin shi ya kare ne a ranar 24/12/16, sannan an nadashi ne domin yiwa kasa baki daya aiki, ba wani bangare na kasa ba, sai gashi yana cutar da yankin Arewa, ya zama wajibi Shugaba Buhari ya dauki matakan dakatar dashi.

No comments:
Post a Comment