Thursday, 13 October 2016

Shi'a: An kashe mutum goma a Katsina




Rahotanni daga jihar Katsina da ke arewacin Najeriya sun ce an kashe akalla mutum goma lokacin da 'yan kungiyar 'yan uwa Musulmi wadda aka fi sani da Shi'a suke juyayin ranar Ashura.
Bayanan da BBC ta samu sun ce lamarin ya faru ne a garin Funtua, lokacin da 'yan sanda da sojoji suka yi yunkurin hana 'yan Shi'ar yin tattaki da suka saba yi duk shekara domin tunawa da ranar ta Ashura.

Wani ganau ya shaida wa BBC cewa ya kirga gawarwakin mutum takwas.
Sai dai babu wata majiya mai zaman kanta da ta tabbatar da wannan ikirari.
Ya kara da cewa an jibge jami'an tsaro a kusa da wurin da suke yin tattakin domin hana su, yana mai cewa jami'an tsaron sun rika harba bindiga sama domin tsorata jama'a.
Da ma dai jihohin Kaduna da Kano da kuma Katsina sun hana 'yan Shi'a yin tattaki a wannan shekarar.
Hasali ma, jihar Kaduna ta haramta kungiyar saboda zarginta da keta dokoki da kuma tayar da zaune tsaye, zargin da suka musanta.







BBC Hausa

No comments:

Post a Comment

Duk Dan Majalisar Da Ya Yi Yunkurin Tsige Buhari A Bakacin Kujerarsa, Cewar Sanata Kwankwaso

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma tsohon ministan tsaro kuma sanatan Kano ta tsakiya a yanzu, Sanata Dakta Rabi'u Musa Kwankwaso yace...